Rana ta
[6]
Shekarar da ka rubuta
2019

Shawara A Rayuwar Musulmi

Allah Ta'ala yana cewa:
"Da kuma wadanda suka amsa kiran Ubangijinsu suka kuma tsai da salla, al'amarinsu kuwa (suna) shawara ne a tsakaninsu, suna kuma ciyarwa daga abin da muka arzuta su". [As-Shura, aya ta 38].
1. A wanan ayar Allah ya bayyana muhimmancin shawara a kan muhimman al’amura na addini da rayuwa.

2. Gwama batun salla tare da na shawara a wuri daya ya nuna cewa duk mai kula da sallarsa yadda ya dace shi ne ya kamata ya zama abokin shawara, domin kuwa shi ne Allah zai tsare shi daga son zuciya da rashin nutsuwa.

3. Yin shawara sananniyar al’ada ce a wurin mutanen Madina, duk sanda wani muhimmin abu ya taso sukan hadu su yi shawara a junansu. Ta hanyar shawara ne suka kai ga cim ma matsayar yin imani da kiran Manzon Allah (SAW) lokacin da wakilansu suka zo musu da labarin da’awarsa daga Makka.

4. Sahabban Annabi (SAW) sun kasance masu haduwa don gudanar da shawara cikin dukkan muhimman al’amuransu. Sun yi shawara lokacin shugabantar da sayyidina Abubakar bayan rasuwar Manzon Allah (SAW), kamar yadda suka yi shawara lokacin yakar masu ridda da sauran al’amura masu yawa. Manzon Allah (SAW) shi ne babban abin koyinsu a nan domin ya kasance mai neman shawararsu a kan abubuwa idan sun taso.

5. Duk abin da Allah da Manzonsa (SAW) suka riga suka yi hukunci a kansa, to babu sauran neman shawarar wani game da daukar wannan hukucin ko rashi daukarsa, kamar yadda Allah ya bayyana cikin Suratul Ahzab, aya ta 36. Sai dai idan al'amari ne da Allah ya bar lokacinsa da mahallinsa a bude, to wannan ana iya yin shawara domin zabar sanda ya dace da inda ya dace a aiwatar da shi, kamar sha'anin Jihadi da sulhu da makamantansu.

6. Neman shawara sunna ce a kan duk wani abu da Allah bai riga ya yi hukunci a kansa ba, kamar al'amuran da suka shafi maslahar al'umma da ta kasa da ta dukiya da tsare-tsaren gudanar da rayuwa ta yau da gobe.

7. Idan Shugaba ya kawo shawara a gaban Musulmi, sai suka hadu a kan ba shi shawara iri daya, to bai halatta ya saba musu ba, domin hakan zai iya jefa al'umma cikin fitina da rarrabuwar kai.

8. Amma idan suka saba a kan lamarin, to idan ya zamanto shi shugaba ne mai ilimi ya kuma san yadda zai dubi al'amarin da iliminsa har ya fita da kyakkyawan ra'ayi, to ya halatta ya saba musu.

9. Amma idan ba mai ilimi ne ba, ko bai san komai game da abin da ya nemi shawara a kai ba, to bai halatta ya saba musu ba, domin idan ya ce zai saba a nan to son zuciya ne zai shigo ciki ba ilimi ba. Allah kuwa ya yi umarni ne da a mayar da al'amari zuwa ga masanansa, domin su ne za su iya tantance abin da ya dace, kamar yadda ya zo a cikin Suratun Nisa'i aya ta 83.
Allah ya sa mu dace. Amin.